Dan Kasar Zimbabwe Ya Auri Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki

top-news

Wata uwa 'yar ƙasar Zimbabwe da ɗanta sun yi ikirarin cewa suna soyayya da juna kuma sun yanke shawarar su yi aure bisa la’akari da cewa mahaifiyar Betty Mbereko (daga Mwenezi a Masvingo) tana da ciki wata shida a yanzu kuma tana jiran haihuwar abin da ke cikinta wanda zai zama ɗanta kuma jikanta.

Mbereko, mai shekaru 40, ta kasance bazawara tun shekaru 12 da suka gabata inda take zaune da ɗanta mai shekaru 23 mai suna Farai Mbereko. Ta tabbatar da cewa tana da ciki wata shida kuma ta yanke shawarar cewa zai fi kyau ta "aure" ɗanta domin ba ta son auren 'yan'uwan mijinta da ya rasu, waɗanda ta ce suna matuƙar kwaɗayin ganin sun aure ta.

Betty ta girgiza wata kotun ƙauye a makon da ya gabata lokacin da ta ce ta fara ƙaunar ɗan nata ne shekaru uku da suka wuce. Ta bayyana cewa ba ta da wani zaɓi sai ta fara neman ɗan nata ya zama mijinta. Farai makaranta bayan rasuwar mahaifinsa, don haka ta ji cewa tana da haqqi a kan kuɗin da yake samu a yanzu domin babu wata mace da ta cancanci hakan.

"Duba da cewa, ni kaɗai na yi masa da gwagwarmaya don in ɗaure ɗana makaranta, ba wanda ya taimaka ni. Yanzu ka ga ɗana yana da kuɗi don haka me za a ce shi za a auri shi sai na yi zarce ni da aikata ba daidai ba? "A bar ni kawai in ji daɗin gumin da na barje," ta faɗa wa kotun ƙauyen. A nashi ɓangaren, ɗan nata, Farai ya ce shi kansa ya fi son ya aure mahaifiyarsa kuma zai biya ragowar bashin sadakin da mahaifinsa ya gada wa ƙakanninsa.

"Na san mahaifina ya rasu kafin ya gama biyan kuɗin sadaki kuma a shirye nake in biya shi," in ji shi.

"Yana da kyau a bayyana abin da muka yi domin mutane su sani cewa ni ne na yi wa mahaifiyata ciki. Idan ba haka ba, za su tuhumeta da fasikanci."

Sai dai kuma, Dagacin ƙauyen, Nathan Mupuitirwa ya ce: "Ba za mu kyale hakan ya faru a ƙauyenmu ba, domin haƙiƙa wannan mummunan al'amari ne). Idan da a zamanin baya suka yi haka, da hakan dole ne a zartar musu da hukuncin kisa amma a yau za mu iya hannun tasu ga 'yansanda."

Ya gargade su da su gaggauta yanke wannan ƙudiri na auren junansu ko kuma su bar ƙauyen da kansu. Tun dai majiyarmu ta bayyana cewa uwar da ɗan sun zaɓi su yi hijira daga ƙauyen inda suka koma wani wuri da ba a bayyana ba.

Majiya: One Africa da Leadership Hausa

NNPC Advert